Gwamnatin Neja ta saka lokacin zaɓen kananun hukumomi

0
44

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Neja ta sanar da ranar 1 ga watan Nuwamba a matsayin lokacin gudanar da zaɓen kananun hukumomin jihar.

Shugaban hukumar Injiniya Mohammed Jibrin Imam, ne ya sanar da hakan lokacin da yake bayyana jadawalin yadda zaben zai kasance a Minna. 

Yace an fara shirin zaɓen a ranar 6 ga watan Maris da muke ciki, yayin da za’a yi zaɓen fidda gwani a tsakanin ranakun 15 zuwa 25 na watan Maris.

Sannan za’a bayyana wadanda za’a tsayar takarar daga 25 ga watan Maris zuwa 2 ga watan Afrilu.

 Imam ya kuma yi alkawarin gudanar da sahihin zaɓe mai cike da adalci ta hanyar yin amfani da ka’idojin da hukumar zaɓen ta gindaya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here