Babban bankin kasa CBN ya naɗa sabbin Daraktoci 16, a manyan sassan sa don inganta yanayin aiki.
Sanarwar da CBN ya fitar tace naɗin sabbin Daraktocin ya fara aiki a ranar 3 ga watan Maris da muke ciki.
Daraktocin sun hadar da Jide-Samuel Avbasowamen, Abdullahi Hamisu, Ojumu Adenike, Makinde Olanrewaju, Sike Ijeoma, Isa-Olatinwo Aisha, Oboh Victor Ugbem, Nakorji Musa, Yusuf Rakiya, Vincent Modesola, Farouk Muhammad, Akinwunmi Olubukola Akinniyi, Solaja Mohammed-Jamiu, Hassan Umar Adedeji da kuma Okpanachi Moses.