Kasashe 10 da suka fi samun ingantacciyar wutar lantarki a Afrika

0
9

Wani rahoto ya nuna cewa wasu kasashe guda goma a nahiyar Afrika sun fi samun aminci da tsayayyiyar wutar lantarki, sakamakon zuba jari a harkar makamashi, fadada hanyoyin samar da wuta da kuma tsare-tsaren gwamnati da suka mayar da hankali kan haɗa jama’a da layin wuta.

A jerin, ƙasashen da suka fi samun wuta ba tare da tangarda ba sun hada da:

1. Masar

Masar tana saman jerin bayan ta cimma kusan kashi 100% na samar da wuta ga dukkan al’ummar ta, ta hanyar haɗa makamashi daga ruwa, iskar gas da sauran su.

2. Morocco

Morocco ma ta kai cikakken kashi 100% na wutar lantarki, ta dogara sosai ga makamashin rana da iska a sabon tsarin canjin ta zuwa sabbin makamashi.

3. Tunisia

Tunisia ta kai matakin 100% na samun wuta, tana amfani da gas da wasu sabbin hanyoyin samar da makamashi.

4. Algeria

Algeria na da kusan kashi 99.8% na samun wuta, a kan tsarin da ya dogara da iskar gas da kuma ci gaba da gyare-gyaren layukan sadarwa.

5. Gabon

Gabon ta kai kashi 91.6%, inda kusan duka biranen ƙasar ke da wuta, sai dai yankunan karkara na ci gaba da fuskantar kalubale.

6. Ghana

Ghana na da sama da kashi 85.9% na samun wuta, tare da dogaro ga ruwa, gas da sauran hanyoyin samar da wuta.

7. Afirka ta Kudu

 Afirka ta Kudu na da kashi 84.4% na samun wutar lantarki, tana ci gaba da saka hannun jari a sabbin hanyoyin samun makamashi.

8. Botswana

Botswana ta kai kashi 72%, inda wutar birane ta fi samun ci gaba fiye da karkara.

9. Kenya

Kenya na da kimanin kashi 71%, na samun lantarki daga ruwa, iska da hasken rana.

10. Senegal

Senegal na da kusan kashi 70% na samun wuta, sannan tana fadada hanyoyin samar da wuta ta hanyar sabbin makamashi da inganta layin sadarwa.

Rahoton ya ce wadannan kasashe sun yi fice wajen aiwatar da tsare-tsaren da suka mayar da hankali kan samar da wuta ga al’umma da dorewa a bangaren makamashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here