Majalisar Wakilan Amurka ta shirya zaman tattaunawa kan zargin cin zarafin Kiristoci a Najeriya

0
5

Majalisar Wakilai ta Amurka ta sanar da shirin ta na gudanar da wani muhimmin taron hadin gwiwa a ranar Talata, domin nazarin rahotannin da ke cewa ana azabtar da Kiristoci a Najeriya.

Sanarwar taron ta fito ne daga ɗan majalisar Amurka, Riley Moore, wanda ya bayyana a shafin sa cewa Mataimakin Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Wakilai kuma shugaban Kwamitin Tsaron Kasa, Mario Díaz-Balart, shi ne zai jagoranci zaman.

An bayyana cewa wasu mambobin Kwamitin Kasafin Kudi da na Harkokin Waje za su taka rawar gani a tattaunawar.

Manufar zaman ita ce tattara hujjoji domin fitar da cikakken rahoto game da kashe-kashen da ake zargin suna afkawa Kiristoci a Najeriya, tare da duba irin matakan da majalisar Amurka za ta ɗauka don taimakawa wajen magance wannan matsala.

Taron na gudana ne a lokacin da ake ci gaba da muhawara tsakanin Amurka da Najeriya kan batun tsaro, sakamakon yawaitar hare-haren ‘yan bindiga da kuma yunƙurin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin kasashen biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here