HomeLocal NewsWHO, UNICEF sun yabawa Kano kan rigakafin corona

WHO, UNICEF sun yabawa Kano kan rigakafin corona

Date:

Related stories

Ganduje sympathises with victims of Kano phone market fire

The National Chairman of the All Progressives Congress (APC),...

Fire destroys over 300 shops in Kano GSM market

A devastating fire has destroyed over 300 shops at...

TikToker remanded over cross-dressing, indecent content in Kano

A popular TikTok content creator, Abubakar Kilina, has been...

Sen Barau donates N22m to bereaved families of Kano athletes

Deputy Senate President, Senator Barau Jibrin, has donated a...
spot_img

Hukumar lafiya ta duniya Who dakuma Asusun tallafawa kananan yara na majalisar dinkin duniya sunyi na’am kan yanda ake gudanar da ayyukan rigakafin cutar Corona a jihar Kano.

Shugaban wata tawagar kungiyoyi masu zaman kansu karkashin hukumomin 2 Tedd Chambe ya bayyana hakan a wata ziyara da suka kaiwa gwamnan jihar Kano dakta Abdullahi Umar Ganduje a gidan gwamnati.

“Mun Kawo ziyara Kano ne domin duba yadda ake gudanar da allurar rigakafin Corona tare da duba yadda zamu iya taimakon jihar Ta fannin rigakafin” a cewar Tedd Chambe.

Da yake jawabi gwamna Abdullahi Umar Ganduje yace babu shakka cutar corona ta taba rayuwar al’umma da dama ta fuskar lafiya da tattalin arziki adon hakane jihar Kano zata cigaba da daukar matakan dakile ta.

Anasa jawabin kwamishinan lafiya Na jihar Kano Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa yace gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bukaci kungiyoyin da su hada karfi da karfe da gwamnatin wajen samar da cibiyar kawo allurar rigakafin corona a jihar domin magance karancin allurar rigakafin a jihar.

Subscribe

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here