HomeLocal NewsWHO, UNICEF sun yabawa Kano kan rigakafin corona

WHO, UNICEF sun yabawa Kano kan rigakafin corona

Date:

Related stories

Kwankwaso honoured with doctorate for championing education in Kano

Former Governor of Kano State and national leader of...

Gov Yusuf probes commissioner linked to release of suspected drug dealer Danwawu

Kano State Governor, Abba Kabir Yusuf, has launched an...

Kano commissioner withdraws surety for drug suspect Danwawu

Kano State Commissioner for Transportation, Alhaji Ibrahim Namadi, has...

Fake EFCC officials jailed in Kano

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial...

Kano govt sends 588 students to 15 states for exchange programme

The Kano State Government has dispatched 588 students to...
spot_img

Hukumar lafiya ta duniya Who dakuma Asusun tallafawa kananan yara na majalisar dinkin duniya sunyi na’am kan yanda ake gudanar da ayyukan rigakafin cutar Corona a jihar Kano.

Shugaban wata tawagar kungiyoyi masu zaman kansu karkashin hukumomin 2 Tedd Chambe ya bayyana hakan a wata ziyara da suka kaiwa gwamnan jihar Kano dakta Abdullahi Umar Ganduje a gidan gwamnati.

“Mun Kawo ziyara Kano ne domin duba yadda ake gudanar da allurar rigakafin Corona tare da duba yadda zamu iya taimakon jihar Ta fannin rigakafin” a cewar Tedd Chambe.

Da yake jawabi gwamna Abdullahi Umar Ganduje yace babu shakka cutar corona ta taba rayuwar al’umma da dama ta fuskar lafiya da tattalin arziki adon hakane jihar Kano zata cigaba da daukar matakan dakile ta.

Anasa jawabin kwamishinan lafiya Na jihar Kano Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa yace gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bukaci kungiyoyin da su hada karfi da karfe da gwamnatin wajen samar da cibiyar kawo allurar rigakafin corona a jihar domin magance karancin allurar rigakafin a jihar.

Subscribe

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here